Close Menu
Good Evening Nigeria…Breaking news in Nigeria
  • News
  • Entertainment
  • Kano
  • International
  • Politics
  • Security
  • Sports
  • More
    • Crime
    • Education
    • Finance
    • Health
    • Kaduna
    • National
    • Nigeria
    • Profile
    • Strategy
    • Technology
Facebook X (Twitter) Instagram
Facebook X (Twitter) Instagram
Good Evening Nigeria…Breaking news in NigeriaGood Evening Nigeria…Breaking news in Nigeria
  • News
  • Entertainment
  • Kano
  • International
  • Politics
  • Security
  • Sports
  • More
    • Crime
    • Education
    • Finance
    • Health
    • Kaduna
    • National
    • Nigeria
    • Profile
    • Strategy
    • Technology
Good Evening Nigeria…Breaking news in Nigeria
Gawuna ya bawa ‘yan wasan Kano dubu dari yayin da gwamnatin Kano ta gaza biyan kudaden gudanar da wasannin PARA
Hausa

Gawuna ya bawa ‘yan wasan Kano dubu dari yayin da gwamnatin Kano ta gaza biyan kudaden gudanar da wasannin PARA

Umar Idris ShuaibuBy Umar Idris ShuaibuDecember 13, 2023No Comments3 Mins Read
Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Ahmad Hamisu Gwale – Abuja

Gwamnatin Kano ta gaza bayar da kudaden Alawus-Alawus ga tawagar da ke wakiltar jihar a gasar cin kofin masu bukata ta musamman ta kasa.

Gasar Masu Bukata ta musamman ta kasa ta wannan shekarar, na ci gaba da gudana a birnin tarayya Abuja da kawo yanzu haka kwana biyu ya rage ayi bikin karkare gasar.

Karanta:

Gwamnatin Kano ta musanta zargin siyar da wani injin dake matatar ruwa ta T/Wada

An dai tsara gasar zata gudana daga 8 zuwa 14 ga Disambar shekarar da muke ciki a filin wasa na Moshood Abiola dake birnin tarayya Abuja.

Wakilinmu ya bamu Labarin cewa wasu cikin wakilan ma’aikatar wasanni, da tawagar Yan Jaridu suna ci gaba da shan wahala sakamakon gaza fitar da kudaden Alawus-Alawus din.

Tin a ranar Asabar aka sanarwa tawagar da zasu wakilci Kano a gasar cewa kudaden gudanarwar ta su zai samu jinkiri zuwa ranar Litinin.

To sai dai yau Laraba da aka shiga kwanaki na biyar babu wani yunkuri daga Gwamnatin jihar Kano kan kudaden da ya kamata a saki domin samun damar gudanar da gasar.

Hakan ta sanya Yan Jaridu da Wakilan ma’aikatar wasanni da kansu suke ciyar da kansu, bayaga yadda suke fuskantar barazana abubuwan yau da kullum domin su gudanar da rayuwarsu.

Wani da ya bukaci a sakaye sunansa ya ce hatta Kundin da Gwamna Abba Kabiru Yusuf ya sanya hannu domin amincewa da sakin kudaden gudanarwar na tawagar ya bata, batare da sanin ina ya shiga ba.

Babu wani yunkuri da aka samu daga Gwamnatin jihar Kano kawo wannan lokaci, domin kawowa tawagar dauki bayan da ya rage Kwanaki a karkare gasar ta wannan shekarar.

To amma Shugaban hukumar wasanni ta jihar Kano Alhali Bala Ya ce suna bakin kokarinsu kan wannan batu, yana mai bayar da tabbacin za suyi duk mai yiwa domin tawagar su samu dauki na gaggawa.

A gefe gudama tsohon Mataimakin Gwamnan Kano Nasiru Yusuf Gawuna da ya samu wakilcin Kabiru Ali Mazadu ya baiwa wasu yan wasan tawagar kyautar Kudi Naira Dubu Dari (100,000).

Gawuna wanda ya bayar da kyautar kudin jim kadan bayan kammala wasan karshe da yan wasan Kwallon guragu na Kano Pillars da yan wasan Pillars Amputee suka samu nasarar lashe Sarkar Zinare a gasar.

Haka Zalika Shima dan kwamitin gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars Alhaji Naziru Wapa, ya bai wa yan wasan Kano Pillars na Para-Soccer da na Pillars Amputee kyautar Naira Dubu Hamsin (50,000).

Spread the love
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn Tumblr Email
Umar Idris Shuaibu

    Related Posts

    Najeriya ta musanta Zarge-Zargen Zagon Kasa da Hukumomin Nijar ke yi Mata

    December 24, 2024

    Zaben Kananan Hukumomi A Kaduna: Jiki Magayi In Kuka Sake Karbar Taliya – Sakon NNPP Ga Masu Kada Kuri’a

    October 18, 2024

    KASSOSA Aji na 88 sun yi taron liyafar cin abinci, sun sha alwashin karfafa zumunci tsakanin mambobi

    July 1, 2024

    Sama da dalibai miliyan 1.2 ne suka amfana da gyara da fadada makarantun sakandare a jihar Kano

    February 3, 2024
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Latest Posts

    Natasha’s Case: ”Senate must remain impartial in handling harassment allegations” – NBAWF

    March 9, 2025

    Hon. Bala Congratulates Ganduje on Tenure Elongation as APC National Chairman

    February 28, 2025

    LG Staff Urged to Remain at Duty Posts to Drive Development

    February 25, 2025

    BREAKING: Lucky Aiyedatiwa Sworn In As Ondo Governor

    February 24, 2025

    El-Rufai Reacts To Tinubu’s Birthday Message

    February 24, 2025
    Advertisement
    © 2025 Good Evening Nigeria
    • Home
    • About Us
    • Contact us
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.